Labarai

‘Yan Sanda Sun Kamo ‘Yan Daba A Kano

Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Kano ta kama mutane 8 cikin wadanda ake zargi sun fito fadan daba tare da jiwa Kansu raunuka, a unguwar kofar Na’isa ranar Alhamis din data gabata. Kakakin rundunar ƴan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana a shafin sa na Facebook , ayau Asabar. Rundunar […]

Read more

Sarakunan Jigawa Sun Taya Gwamna Namadi Murnar Samun Lambar Yabo

Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi FCA, ya karbi bakuncin sarakunan jihar su biyar, wadanda uku daga cikinsu suka samu wakilcin hakimansu karkashin jagorancin shugaban majalissar sarakuunan jihar, Mai Martaba Alhaji Adamu Abubakar Make Haruna CON Sarkin Hadejia. Ziyarar sarakunan na zuwa ne bayan dawowar gwamna Namadi Umar, daga bikin karbar lambar yabon da ya […]

Read more

Gwamnatin Nijar Ta Rusa Kungiyoyin Kwadago

Gwamnatin mulkin soji a jamhuriyar Nijar ta rusa ƙungiyoyin ƙwadago guda uku da ke wakiltar jami’an tsaro da suka haɗa da na ma’aikatan kwastam da na ma’aikatar kula da ruwa da gandun daji. Wannan na ƙunshe cikin wata sanarwar da ma’aikatar harkokin cikin gida ta fitar. Hukumomin sun ɗauki wannan mataki ne kamar yadda kundin […]

Read more

Gwamnatin Kano Ta Mika Bayanan Wadanda Aka Kashe A Edo

Gwamnatin jihar Kano ta ce ta kammala tattara bayanan iyalan mutanen da aka kashe a Uromi da ke jihar Edo inda ta mika wa gwamnatin Edon sunayensu. Tun da farko gwamnatin jihar ta Kano ta kafa kwamiti da zai gudanar da bincike tare da tattara bayanan iyalan mafarautan da aka kashe. Mataimakin gwamnan jihar ta […]

Read more

Harajin Trump Ba Zai Sa Mu Mika Wuya Ba – China

China ta dage cewa ba za ta mika wuya ba, duk da matsin da take fuskanta daga shugaba Trump na lafta mata haraji, amma ta ce idan an nemi ayi sulhu a shirye take. Ma’aikatar kasuwancin kasar ta ce kofar tattaunawa a buɗe take. Rahotanni sun ce dama sun jima cikin shiri, sannin cewa irin […]

Read more

Kotu Ta Sanya Alpha Chales A Hannun Beli Kan Zargin Bata Suna

Kotun Majistret mai lamba 17 karkashin jagoranci mai Shari’a Huda Haruna Abdu, ta bayar da belin matashiyar yar Tiktok din nan Alpha Charles, wadda Ƴan Sanda suka gurfanar a gaban bisa zargin ta da laifin ɓata suna. Ƙunshin zargin ya bayyana cewar Alpha Charles, ta ɓata sunan Sadiya Haruna ta dandalin sada zumunta. Yayin da […]

Read more