Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr
Babban Daraktan Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahamed Umar Labbo, ya taya Gwamna Umar Namadi da al’ummar jihar murnar kammala azumin watan Ramadan cikin nasara. A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Hukumar, Habibu Yusuf Babura, ya fitar a ranar Alhamis, Labbo ya bayyana cewa Eid-el-Fitr wata muhimmiyar rana […]