Labarai

Shugabannin Turai sun yi wa Trump tawaye kan yaƙin Iran

Karin wasu shugabannin Turai sun yi watsi da buƙatar Shugaban Amurka Donald Trump ta neman taimako wajen tabbatar da tsaron zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigin Hormuz, da Iran ta rufe. Bayan wani taron ministocin harkokin wajen Tarayyar Turai, babbar jami’ar kula da manufofin ƙasashen waje ƙungiyar, Kaja Kallas, ta ce “babu wanda ke son yin […]

Read more

Tinubu ya umarci hafsoshin tsaro su koma Maiduguri

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bai wa hafsoshin tsaro umarnin komawa Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, domin su jagoranci ayyukan tsaro kai tsaye a yankin. Wannan mataki ya biyo bayan hare-haren bama-bamai da suka yi sanadin mutuwar mutane sama da 20 tare da jikkata fiye da 100. Rahotanni daga Maiduguri sun bayyana cewa wasu da […]

Read more

An yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu da Iran a Birtaniya

Ɗaruruwan mutane sun gudanar da zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu a birnin Landan na Birtaniya, duk da cewa gwamnati ta haramta gudanar da gangamin jama’a saboda dalilan tsaro. ’Yan sanda sun ce an kama mutum 12 yayin zanga-zangar, tare da buɗe bincike kan wasu kalaman adawa da Isra’ila da aka yi a wajen gangamin. Ministar harkokin […]

Read more

Abin da ya sa na koma APC – Gwamnan Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa rikicin cikin gida da kuma shari’o’in da suka dabaibaye tsohuwar jam’iyyarsa ta PDP ne babban dalilan da suka sa ya fice daga jam’iyyar zuwa APC. A ranar Litinin ne gwamnan ya sanar da sauya sheƙarsa daga PDP zuwa jam’iyya mai mulki ta APC a hukumance bayan wani […]

Read more