Labarai

Najeriya na ƙara sa ido bayan ɓarkewar Ebola a Congo

Hukumar Daƙile Yaɗuwar Cututtuka a Najeriya, NCDC ta ce duk da cewa ba a samu ɓullar cutar Ebola ba a ƙasar, tana ƙarfafa matakai don sa ido sakamakon mutuwar mutum 88 a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo da kuma samun mutum guda da aka bayar da rahoton ya kamu da cutar a Uganda. Cikin wata sanarwa da […]

Read more

Kotu ta ba da belin El Rufai kan naira miliyan 100

Wata babbar kotun tarayya a Abuja ta bayar da belin tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El Rufai. An bayar da belinsa ne kan naira miliyan 100 da mutum guda da zai tsaya masa kan makamancin kuɗin. Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta bayyana tsauraran ƙa’idodin belin inda ta ce wanda zai tsaya masa dole ne […]

Read more

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Shugaban hukumar shigi da fici ta Najeriya mai ritaya kuma jigo a jam’iyyar APC, Muhammad Babandede, ya ziyarci iyalan tsohon ɗan majalisar wakilai, Hon. Abba Anas Adamu Laushi, wanda ya rasu a hannun masu garkuwa da mutane. Babandede ya bayyana rasuwar marigayin a matsayin babban rashi ga iyalansa, al’ummarsa da kuma abokan siyasarsa, yana mai […]

Read more

Sanata ya bar APC a jajibirin zaɓen fidda gwani a Kebbi 

Sanatan Kebbi ta Kudu a Majalisar Dattawa, Garba Musa Maidoki, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar APC. A cikin wata wasiƙa da ya aike wa Shugaban APC na mazaɓar Rafin Zuru mai ɗauke da kwanan watan 14 ga Mayu, 2026, Sanatan ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon rikice-rikicen cikin gida da suka dabaibaye jam’iyyar. […]

Read more

An kama ɓarauniyar jariri a asibiti a Zamfara.

An kama wata matashiya ’yar shekara 27, kan zargin satar jariri mai kwana 10 da haihuwa a Babban Asibitin Ƙaura Namoda da ke Jihar Zamfara. Dubun wadda ake zargin ya cika ne kwanan da sace jaririn, inda ’yan sanda suka fara gudanar da bincike bayan samun rahoton. Bayanan samun ƙorafin ne Babban Ofishin ’Yan Sanda […]

Read more