Labarai

Sojoji sun ceto mutum 48 da aka sace a Zamfara

Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta Operation FANSAN YAMMA sun ceto mutum 48 da aka yi garkuwa da su bayan sun fatattaki ’yan bindiga da suka kai hari ƙauyen Magami da ke Ƙaramar Hukumar Kaura Namoda a Jihar Zamfara. Sojojin sun ce sun samu kiran neman agaji da sanyin safiyar Lahadi cewa wasu ’yan bindiga masu […]

Read more

Yan bindiga sun sace shugaban ƙaramar hukuma a Zamfara

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu ta Jihar Zamfara, Alhaji Nura Umar Bungudu, bayan sun kai hari gidansa cikin dare a ranar Alhamis. Rahotanni sun ce maharan sun kawo harin ne har cikin garin Bungudu, inda suka nufi gidan shugaban ƙaramar hukumar da ke unguwar Zango, kusa da […]

Read more

Yar Najeriya ta kammala jami’ar Burtaniya da daraja ta daya (1st Class) a ilimin kimiyar samar da manhajar kasuwancin zamani.

Yar Najeriya, Zainab Muhammad Babandede, ta sake ɗaga martabar ƙasarta, inda ta kammala karatun digirin farko (BSc) a fannin Kimiyyar Samar Da Manhajar Kasuwancin Zamani (Engineering Software for Business) da matsayin Daraja ta Farko (First Class) a Jami’ar University of the West of England (UWE), Bristol, da ke Birtaniya. Wannan gagarumar nasara ta ƙara tabbatar […]

Read more