DSP Hussaini Abdullahi Ya Zama Sabon Mai Magana Da Yawun Rundunar Yan Sandan Shiya Ta Daya Zone One Kano.

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta sanar da naɗe-naɗen sabbin masu magana da yawun rundunar wasu shiyyoyi, ciki har da naɗin DSP Hussaini Abdullahi a matsayin sabon mai magana da yawun rundunar yan sandan shiya ta daya wato Zone 1, Kano.

DSP Hussaini Abdullahi, wanda ya maye gurbin CSP Bashir Muhammad, ya kasance mataimakin kakakin rundunar yan sandan Jihar Kano, kafin wannan naɗin.

Rahotanni na cewa kwarewarsa da jajircewarsa wajen hulɗa da jama’a ne suka tabbatar da cancantarsa ga sabon matsayin da ya samu.

A cewar takardar naɗin, rundunar ta kuma nada wasu sabbin jami’an hulɗa da jama’a a wasu shiyyoyi na ƙasar, domin ƙarfafa sadarwa da inganta isar da sahihan bayanai, da tabbatar da cewa al’umma suna samun cikakkun rahotanni kan aiyukan tsaro a yankunansu.

Rundunar ta bayyana cewa waɗannan nade-nade na cikin tsarin sabunta shugabanci da ƙarfafa aikin hulɗa da jama’a a matakai dabam-daban.

Al’umma da dama sun taya sabbin kakakin murna tare da fatan Allah ya ba su nasara a sabbin ayyukan da aka dora mu su.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda