DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara

Hukumar Tsaro ta DSS ta kama wani likita da ake zargin yana ba da magunguna tare da kula da ’yan bindiga masu garkuwa da mutane da ke wasu sassan jihar Kwara.

An kama wanda ake zargin, wanda ba a iya gano sunansa ba a lokacin rahoton, a yankin Jebba bayan rahotannin sirri sun nuna cewa wasu masu safarar kaya suna kai magunguna daga Sakkwato domin kula da ’yan fashin daji da suka samu raunuka a dazukan jihar.

Majiyoyin tsaro sun ce da dama daga cikin waɗannan ƙungiyoyin masu laifi sun samu raunukan harbin bindiga a fafatawar da suka yi da jami’an tsaro a baya-bayan nan.

“Saboda haka muna ba da shawarar ƙara tsaurara matakan tsaro a cibiyoyin lafiya da ke cikin dazuka, domin masu garkuwa da mutane na iya kai hari a wuraren,” in ji wani jami’in tsaro.

Mai magana da yawun gwamnan jihar ta Kwara, Rafiu Ajakaye, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa kamun wata babbar nasara ce a ƙoƙarin da ake ci gaba da yi kan ’yan fashin daji.

“Wannan babban mataki ne daga DSS. Ya ƙara tabbatar da cewa hukumomin tsaro suna matsawa wa waɗannan ’yan ta’adda, suna kuma toshe hanyoyin tallafi da ke ba su damar gudanar da ayyukansu,” in ji shi.

Ajakaye ya ƙara da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da ƙarfafa haɗin gwiwa da hukumomin tsaro domin rufe dukkan hanyoyin da ke taimaka wa ayyukan garkuwa da mutane.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda