Home » Galadiman Kano Abbas Sunusi Ya Rasu

Galadiman Kano Abbas Sunusi Ya Rasu

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

 

Rahotanni na cewa Allah Ya yi wa Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sunusi ya rasuwa bayan fama da jinya.

Wata sanarwa da ta fito daga cikin iyalansa ta tabbatar da rasuwar, inda ta ce nan gaba za a bayyana lokacin da za a yi masa jana’iza  Kofar Kudu da ke Gidan Rufma .

Galadiman Kano ya rasu yana da shekaru 92 kuma shi ne dattijo mafi tsufa a duk Masarautar Kano

Alhaji Abbas Sunusi kawu ne ga Sarki Muhammadu Sunusi II, kuma mahaifi ga shugaban jam’iyyar APC na Kano, Abdullahi Abbas.

Marigayin shi ne Wamban Kano babban ɗan majalisar Sarki kafin daga likafar sarautarsa zuwa Galadiman Kano.

Tun a shekarun 1950 Abbas Sanusi ya zama mamba a majalisar Masarautar Kano, inda a karon farko mahaifinsa, Sarki Sanusi I, ya naɗa masa rawanin Sarkin Dawakin Tsakar Gida kuma Hakimin Ungogo a shekarar 1959.

A shekarar 1962 kuma Ɗan Iyan Kano a zamanin mulkin Sarki Muhammadu Inuwa, sannan ya zama Wamban Kano a lokacin Sarki Ado Bayero.

A lokacin mulkin Sarki Muhammadu Sunusi II na farko ne aka ɗaga likafarsa zuwa Galadiman Kano.

An haifi Abbas Sanusi a shekarar 1933 a garin Bichi, inda ya soma karatunsa a Makarantar Ƙofar Kudu a shekarar 1944, sannan a shekarar 1948 ya tafi Makarantar Kano Middle School da a yanzu ake kira Rumfa College.

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?