Home » Gwamanatin Jigawa Za Ta Taimaki Masu Bincike Akan Ciwon Ƙoda

Gwamanatin Jigawa Za Ta Taimaki Masu Bincike Akan Ciwon Ƙoda

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Gwamnatin jihar Jigawa ta yi alƙawarin taimakawa masana masu bincike akan ciwon ƙoda da ke addabar jama’ar wasu yankuna a jihar. 

Kwamishinan lafiya a ji Jigawa, Honorabul Dokta Muhammad Abdullahi Kainuwa ne ya bayyana hakan a wani taron wayar da kai akan ciwon ƙoda a Haɗejia.

Kungiyar Likitoci ta Najeriya ne dai ta shirya taron a garin Haɗejia, ɗaya daga cikin yankunan da ke fama da samun mutane masu ciwon ƙoda.

Kainuwa ya bayyana cewa zai yi amfani da damarsa, wurin haɗa masu niyyar yin bincike mai zurfi akan ciwon ƙoda da waɗanda za su ɗauki nauyin binciken.

Ya ce zurfafa bincike akan ciwon ƙoda zai taimaka wurin magance ciwon cikin gaggawa.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?