Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sabon Sarkin Zuru

Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris ya amince da nadin Alhaji Sanusi Mika’ilu a matsayin sabon sarkin Zuru.

Cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran gwamnan, Ahmed Idris ya fitar ya ce gwamnan ya amince da naɗin ne sakamakon shawarar kwamitin zaɓen sabon sarkin.

Yayin da yake miƙa wa sabon sarkin takarakar nadin kwamishin ƙananan hukumomi da masarautun gargajiya na jihar, Hon. Garba Umar Dutsin-Mari ya buƙaci sabon sarkin ya nuna halin dattakon da aka tsammata daga gare shi.

Naɗiin sabon sarkin na zuwa ne bayan mutuwar tsohon sarkon Marigayi, Alhaji Muhammad Sani Sami wanda ya rasu ranar 16 ga watan Agustan da muke ciki.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda