Gwamnatin Kano za ta fara raba wa ɗalibai mata tallafi

Gwamnatin Kano ta bayyana cewa ta fara shirin raba Naira dubu ashirin ga dalibai mata dubu arba’in da biyar a matsayin tallafi domin ƙarfafa wa iyaye su riƙa tura ‘ya’yansu makaranta.

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ne ya bayyana hakan a yayin gudanar da bikin ranar samun ‘yancin Najeriya karo na sittin da uku da aka yi a Sani Abacha Stadium.

Ya kuma ce za a dawo da motocin da ke kai yara mata zuwa makaranta tare da dawo da su unguwanninsu.

Sannan gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta gina karin makarantu a ƙananan hukumomi 44 da ke jihar nan domin rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta ko da ke yawa a tituna.

A irin wannan yunƙuri ne, gwamnatin ta shirya aikewa da ɗalibai dubu ɗaya da ɗaya ketare domin yin digiri na biyu da suka samu sakamakon mai daraja ta ɗaya a digirinsu na farko.

Post masu alaƙa

Sojojin Najeriya sun ceto mutane 9 daga masu garkuwa a Kogi.

Kotu tsare mutane biyu da ake zargi da rushe Gadar Watari da yanka filaye ba bisa ka’ida ba a Kano.

Rundunar yan sandan Kano ta kwato motar da aka sace sannan aka siyar da ita a Nijar