Zaɓe: Kotu ta soke nasarar da gwamnan Nassarawa ya samu

Kotun sauraron ƙararraki zaɓen gwamnan Kano a jihar Nassarawa, ta umarci hukumar zaɓen jihar da ta janye shaidar samun nasarar lashe zaɓen gwamnan da Injiniya Abdullahi Sule na jam’iyyar APC ya yi a zaɓen da aka yi na ranar 19 ga watan Maris ɗin shekarar da muke ciki.

Sannan kotun ta umarci hukumar zaɓen da ta ayyana David Ombugadu na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya samu nasarar.

Wannan umarni ya fito ne daga bakin mai shari’a Ezekiel Ajayi wanda ya bayyana hakan a yau.

A yayin da yake bayyana jin daɗinsa, tsohon shugaban majalisar Dattawan ƙasar nan, Bukola Saraki, ya taya ɗan jam’iyyar tasu ta PDP murnar wannan nasara da ya samu a kotun.

Wannan hukunci na zuwa ne bayan an yi makamancinsa a nan Kano inda kotun ta ayyana Dr. Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaɓen Kano, a maimakon gwamnan Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf wanda tuni ya tabbatar da shirinsa na ɗaukaka ƙara.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr