Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun hutu

Gwamnatin Tarayya ta bayyana ranar 29 ga wannan wata na Maris da kuma 1 ga watan Afrilu a matsayin ranakun hutun Good Friday da Easter Monday.

Ministan cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana haka a madadin Gwamnatin Tarayya a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Babbar Sakatariyar Ma’aikatar, Aishatu N’dayako.

Tunji-ojo ya yi amfani da wannan damar ya yi kira ga mabiya addinin Kirista da ma ƴan ƙasa baki ɗaya su yi koyi da karantarwa Yesu Almasihu kamar yadda ya nuna a rayuwarsa.

Post masu alaƙa

Kotun kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kwace kadarorin Godwin Emefiele

Dalibai huɗu za su wakilci Najeriya a gasar Spelling Bee ta Duniya a China

Babandede Ya Taya Shettima Murnar Sake Samun Takarar Mataimakin Shugaban Kasa