Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun hutu

Gwamnatin Tarayya ta bayyana ranar 29 ga wannan wata na Maris da kuma 1 ga watan Afrilu a matsayin ranakun hutun Good Friday da Easter Monday.

Ministan cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana haka a madadin Gwamnatin Tarayya a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Babbar Sakatariyar Ma’aikatar, Aishatu N’dayako.

Tunji-ojo ya yi amfani da wannan damar ya yi kira ga mabiya addinin Kirista da ma ƴan ƙasa baki ɗaya su yi koyi da karantarwa Yesu Almasihu kamar yadda ya nuna a rayuwarsa.

Post masu alaƙa

Hisbah ta fara horas da sabbin jami’anta a Jigawa

Dan KAROTA da direba ya buge ya gudu Nasiru Abdullahi Mai Jihadi ya rasu ya bar mata 2 da ‘ya’ya 12.

An kama budurwa ‘yar shekara 15 kan safarar miyagun kwayoyi a Delta.