Home » Gwamnatin Tarayya Ta Gargadi Masu Kirkirar Bidiyon Bola Tinubu Na Bogi

Gwamnatin Tarayya Ta Gargadi Masu Kirkirar Bidiyon Bola Tinubu Na Bogi

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Ministan yaɗa labaran Najeriya Mohammed Idris ya gargaɗi ƴan ƙasar kan amfani da ƙirƙirarrun bidiyo domin nuna shugabannin ƙasar a wani yanayi mara kyau domin ɓata musu suna.

Jaridar The Nation mai zaman kanta ta ruwaito ministan yana cewa, “mun ga yadda ake amfani da ƙirƙirarriyar basira ta hanyoyin da suka dace, da hanyoyin da ba su dace ba. Zai iya yiwuwa kana zaune a nan kawai sai wani ya yanko kanka ya ɗaura a wani jikin domin ɓata maka suna.”

“Muna ganin yadda ake juya maganar shugaban ƙasa, inda zai faɗa abu daban, amma sai a canja abin da ya faɗa. Ko kuma minista ya faɗa wani abu, sai a juya masa magana,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa suna duba lamarin sosai a matakin gwamnati, “musamman yadda za mu tsaftace kafofin sadarwa ba tare da tauye haƙƙin furta albarkacin baki ba.”

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?