Hamɓararren shugaban ƙasar Guinea Bissau ya isa makwabciyar ƙasarsa, Senegal bayan wata yarjejeniya da kungiyar ECOWAS ta jagoranta.
Wakilin BBC ya ce ma’aikatar harkokin wajen Senegal ta ce a ranar Alhamis da yamma wani jirgin sama na soji ya sauka a ƙasar da Mista Embalo a ciki.
A shekaran jiya Laraba ne sojoji suka hamɓarar da Umaro Sissoco Embaló, da sauran jami’ai daga mulki – kwana ɗaya kafin bayyana sakamakon zaben shugaban ƙasar da aka yi.
Da dama na ganin Mr Embaló ne zai yi nasara a zaben na kasar ta yammacin Afirka.
An rantsar da shugaban rundunar sojin ƙasa ta ƙasar a matsayin shugaba na abin da sojojin suka kira gwamnatin rikon-ƙwarya.