Hukumar Civil Defense Zata yi bincike kan zargin mutawar matashi a ofishinta dake Kano.

Rundunar tsaro ta Civil Defense reshen jihar Kano, ta ce, za ta yi ƙwaƙƙwaran bincike kan zargin kashe wani matashi mai suna, Halifa Abdullahi, a ofishin rundunar na ƙaramar hukumar Fagge.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, SC Ibrahim Idris Abdullahi, ne ya bayyana hakan, a ranar Alhamis, biyo bayan yadda a ka zargi jami’an rundunar a ofishin na Fagge da sanadiyyar rasuwar matashin da ke taimaka musu a jiya Laraba 8 ga Janairu, 2026.

SC Ibrahim Idris, ya ce, yanzu haka shugaban rundunar ya kafa wani kwamiti, domin gudanar da bincike, domin tabbatar da adalci a kan al’amarin.

Ya kuma ce, kwamitin da aka kafa zai yi aiki ne tare da rundunar ƴan sandan jihar Kano, domin ganin an zurfafa bincike tare da ɗaukar matakin da ya dace a kan al’amarin.

Post masu alaƙa

CP Ibrahim Bakori ya kai gaisuwar ban-girma ga Sarkin Karaye tare da halartar bikin rantsar da yan NYSC.

Yan Sanda Sun Kama Ɓarayin Wayar Lantarki A Katsina

Buga fasfo ne aka mayar Abuja, ba karɓarsa ba – Immigration