Hukumar kiyaye hadura ta kasa reshen jihar Kano,( FRCN) ta tabbatar mutuwar mutane 21 yayin da mutane 11 suke asibiti don samun kulawar likitoci, sakamakon mummunan hadarin da ya faru da tawagar yan wasan Kano, bayan kammala halattar gasar wasanni ta kasa (NSF) da aka gudanar a jihar Ogun, inda motarsu ta fada kasan wata Gada a yankin Dakatsalle karamar hukumar Kura, kan hanyarsu ta dawo wa gida yau asabar.
Kakakin hukumar kiyaye hadura ta kasa reshen jihar Kano, CRC Abdullahi Aliyu Labaran, ne ya tabbatar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya aikewa da manema labarai.
- Yau Ce Ranar Bikin Yaki Da Shan Taba Sigari A Duniya.
- 20 Daga Cikin Tawagar Yan Wasan Kano Sun Rasu Akan Hanyar Dawo Wa Gida
Sanarwar ta ce bayan samun mummunan labarin jami’ansu sun garzaya inda lamarin ya faru , tare da kai wadanda suka jikkata asibitin kwararru na Murtala Muhammed da kuma gwawarwakin.
Hukumar ta mika sakon ta’aziyarta ga gwamnatin jihar Kano da iyalan mamatan harma da al’ummar jihar baki daya kan iftila’in hatsarin motar da yayi sanadiyar rasuwar matasan tare yin addu’ar samun lafiya ga wadanda suka jikkata.
Haka zalika hukumar ta yi kira ga al’ummar jihar Kano dama masu ababen hawa da su dinga kiyayewa da dokokin tuki a koda yaushe.