INEC na shirin cire NDC daga rajistar jam’iyyun siyasa bayan hukuncin kotu

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) na shirin cire jam’iyyar NDC daga jerin jam’iyyun da ta amince da su, bayan wani hukuncin Kotun Tarayya da ya soke umarnin da ya tilasta mata yin rajistar jam’iyyar a baya.

INEC ta bayyana cewa ta nemi kwafin hukuncin kotun (CTC), inda ta ce za ta aiwatar da abin da kotu ta yanke da zarar ta samu shi.

Ta ƙara da cewa kafin hukuncin da aka yanke a watan Disambar 2025, ta riga ta ƙi amincewa da buƙatar NDC na yin rajista a matsayin jam’iyya.

Alƙalin Kotun Tarayya da ke Lokoja, Mai Shari’a Isah Dashen, ne ya soke hukuncin da aka yanke a baya, inda aka umarci INEC ta yi wa NDC rajista.

Yanzu ana sa ran komawa kotun domin sake sauraron shari’ar kafin a yanke hukunci na ƙarshe.

Post masu alaƙa

Kwastam ta kama harsasai 3,300 da kayayyakin fasa-ƙwauri a Seme

Jigawa na da ƙarfin samar da sama da kashi 50 cikin 100 na buƙatar shinkafar Najeriya – Shugaban NUJ

Ba na tsoron duk wata barazana daga Gwamnatin Tarayya a yayin zaɓen Osun — Gwamna Adeleke