Jamhuriyar Nijar Ta Fice Daga Kawancen Yakar ‘Yan Ta’addan Boko Haram

Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar karkashin jagorancin Janar Abdurrahmane Tchiane ta bayyana janye dakarunta daga rundunar Hadin Gwiwa mai yaki da Boko Haram a yankin Tafkin Chadi.
Gwamnatin ta ce ta  janye dakarun nata ne domin mayar da hankali wajen tabbatar da tsaron bututun mai na ƙasar da ke fuskantar hare-haren ƴan bindiga.
Wannan mataki na gwamnatin jamhuriyar Nijar ya zo wa mutane da dama da fuskoki daban daban inda wasu ke ganin an yi dai dai, wasu kuma ke ganin akasin haka.
A baya bayan nan ne dai aka tabbatar wa Janar Abdurrahmane Tchiane wa’adin mulki na shekara biyar, inda ake sa ran kafin wannan lokacin, zai inganta rayuwar kasar da ‘ya’yanta.

Post masu alaƙa

Ƴan sandan Kano za su ƙara ƙaimi wajen amsa kiran gaggawa – CP Bakori

Masu Garkuwa Da Janar Rabe Na Neman A Sako ’Yan Bindigar Da Ke Hannun Gwamnati

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu