An Sa Dokar Hana Fita A Mazabar Sanata Natasha

Rahotanni daga karamar hukumar Okehi a jihar Kogi, mazabar Sanata Natasha Akpoti, na cewa Shugaban karamar Hukumar Amoka Monday, ya sanya dokar hana fita, saboda matsalar tsaro biyo bayan hana tarukan siyasa da na jama’a ba bisa ka’ida ba.

A cikin wata sanarwa da shugaban ya fitar a ranar Litinin, ya bayyana cewa sanya dokar hana fita ya zama wajibi domin wanzar da zaman lafiya da kuma bin umarnin gwamnatin jihar Kogi da kuma kwamishinan ‘yan sandan jihar.

Sanarwar ta kara da cewa, duk wanda aka samu yana taro ko kuma hada mutane ba tare da izini daga hukumomin da abin ya shafa ba za a kama shi kuma za a gurfanar da shi a gaban kotu.

Wanna na kunshe a cikin wani rahoto da kafar yada labarai DCL Hausa ta wallafa.

Post masu alaƙa

Sojojin Najeriya sun daƙile yunƙurin garkuwa da mutane tare da ceto mutum 23

Dan KAROTA da direba ya buge ya gudu Nasiru Abdullahi Mai Jihadi ya rasu ya bar mata 2 da ‘ya’ya 12.

An kama budurwa ‘yar shekara 15 kan safarar miyagun kwayoyi a Delta.