Katsina: Ɗan Takarar PDP Ya Ƙi Amincewa da Sakamakon Zaɓe

Dan takarar gwamnan jihar Katsina na babbar jam’iyyar adawa ta PDP, a zaben da ya gabata, Sanata Yakubu Lado Dan Marke, ya bayyana rashin amincewarsa da sakamakon zaben da hukumar zabe ta bayyana.

Dan takarar gwamna na jam’iyyar ta PDP, ya ce, ya kamata a daina yin zabe kawai a rinka yin nadi, don yana ganin hakan ya fi dacewa.

Sanata Lado Dan Marke, ya ce “‘Yar manuniya ta nuna ko a lokacin yakin neman zabe, domin duk inda jam’iyyar APC ta je kampe ba ta ji da dadi ba saboda mutane sun gaji da ita, amma  duk inda  PDP ta je maraba ake yi da ita.

Ya ce, su ba za su yi wani abu da zai saba wa doka ba, za su yi abin da doka ta tanada, saboda haka mutane su kwantar da hankulansu za a yi duka abin da ya dace don kwatowa al’ummar jihar katsina hakkinsu.

Post masu alaƙa

Ƙungiyoyin PDP 293 sun koma APC a Yobe

An samu ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a a zaɓen cike gurbi a Kano

APC ta fara faɗawa tarkon rikici a jihar Kano