Dan Takarar PDP Ya Kada Gwamna Mai Ci a Jihar Zamfara

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a jihar Zamfara ta bayyana Dauda Lawal Dare a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar.

Dauda Lawal dai ya samu ƙuri’u 377,726 – inda ya yi nasara a kan gwamna mai ci Bello Muhammad Matawalle wanda ya samu ƙuri’u 311,976.

An dai kwashe tsawon lokaci ana tattara sakamakon zaɓen biyo bayan jinkiri da aka samu.

Rahotanni da suka fito daga jihar sun ce an sace jami’an tattara sakamakon zaɓe a kan hanyarsu ta zuwa Gusau, babban birnin jihar, daga ƙaramar hukumar Maradun.

Sai dai rahotonni sun nuna cewa an saki jami’an daga baya.

Post masu alaƙa

Barau Ya Zama Ɗan Takarar Sanatan Kano Ta Arewa A APC

Sanata ya bar APC a jajibirin zaɓen fidda gwani a Kebbi 

Yusuf Buhari ya lashe zaɓen takarar majalisar tarayya a APC