Labari Cikin Hotuna: Yadda Aka Gudanar da Sallar Idi a Masallacin Ƙofar Mata

An gudanar da sallar Idin ne da misalin ƙarfe 8:30 na safe wanda limamin Kano Farfesa Sani Zahraddeen ya jagora.

Farfesa Sani Zahraddeen

Mai martaba sarkin Kano, Alh. Aminu Ado Bayero, ya halarcin sallar tare da hakimansa da sauran manyan hadimansa.

Mai martaba sarkin Kano, Alh. Aminu Ado Bayero

Haka shi ma mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, na cikin manyan jami’an gwamnatin jihar Kano da suka halarci salla a masallacin.

Sannan akwai mutane kamar sanata Kabiru Gaya da shugaban Hukumar Karota, Baffa Babba Dan’Agundi da Ali Baba a Gama Lafiya da sauransu.

Post masu alaƙa

Sojojin Najeriya sun ceto mutane 9 daga masu garkuwa a Kogi.

Kotu tsare mutane biyu da ake zargi da rushe Gadar Watari da yanka filaye ba bisa ka’ida ba a Kano.

Rundunar yan sandan Kano ta kwato motar da aka sace sannan aka siyar da ita a Nijar