Majalissar Dattawan Nijeriya Zata Tantance Sabbin Hafsoshin Tsaro A Ranar Laraba

A gobe Laraba ne majalisar dattawa ta Najeriya za ta tantance sababbin manyan hafsoshin tsaron ƙasar da Shugaba Bola Tinubu ya naɗa.

Tinubu ya aike da sunayen sababbin hafsoshin ne zuwa ga majalisa domin tantancewa kamar yadda kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada.

Shugaban majalisar Sanata Godwill Akpabio ya tabbatar da karɓar wasiƙar ta shugaban ƙasa, inda ya ce kwamitin da ke da alhakin aikin zai zauna gobe ya tantance su.

Tinubu dai ya yi sauye-sauye ne a ɓangaren tsaron ƙasar, inda ya ɗaga darajar Laftanar Janar Oluyede Olupemi daga babban hafsan sojin ƙasa zuwa babban hafsan tsaron ƙasar domin ya maye gurbin Janar Christopher Musa wanda aka cire.

Sannan ya naɗa sababbin hafsoshin sojin sama da na ruwa da ƙasa, sannan ya bar babban hafsan sashen tattara bayanan sirri na sojin ƙasar, Manjo Janar E.A.P. Undiendeye

Related posts

Tinubu Ya Cire Sunan Maryam Sanda Daga Waɗanda Ya Yi Wa Afuwa

Ba Daidai Ba Ne Tinubu Ya Ci Gaba Da Ciyo Bashi Duk Da Cire Tallafin Mai – Sanusi

Yan Sanda Dubu 45,000 Ne Za Su Kula Da Zaben Jihar Anambra