Home » Mayaƙan Boko Haram 50 Sun Baƙunci Lahira A Kaduna 

Mayaƙan Boko Haram 50 Sun Baƙunci Lahira A Kaduna 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Jami’an hukumar tsaro ta Sibil Difens sun aika mayaƙan Boko Haram kimanin 50 barzahu yayin musayar wuta a Jihar Kaduna.

Hukumar NSCDC ta bayyana cewa, mayaƙan na Boko Haram sun gamu da ajalinsu ne bayan sun yi wa jami’anta kwanton ɓauna ranar Litinin.

Kakakin Hukumar Sibil Difens, Babawale Afolabi, ya ce jami’an hukumar sun yi arangama da mayaƙan ne a lokacin da suke sintirin kare babban layin wutar lantarki da ya taso daga yankin Shiroro a Jihar Neja.

Babawale Afolabi ya ce “Mayaƙan Boko Haram kimanin 200 ɗauke da muggan makamai ne suka kai wa jami’an mu kusan su 80 hari a yankin ƙauyen Farin Ruwa da ke Ƙaramar Hukumar Cikun da ke Jihar Kaduna.

“Daga ganin ayarin motocin jami’an suka buɗe musu wuta, saboda wai ayyukan jami’an tsaron sun takura musu a yankin.

“Amma jami’an namu sun yi nasarar halaka 50 daga cikin maharan, ko da yake ba a ga mutum bakwai daga cikin jami’an namu ba tukuna. Akwai wasu kuma da suka samu raunuka a yayin musayar wutar,” .

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?