Najeriya na shirin ɗaukar jami’an tsaro 90,000 kan matsalar tsaro

Gwamnatin Najeriya ta bayyana shirin ɗaukar sama da jami’an tsaro 90,000 a wani sabon mataki na ƙarfafa yaki da matsalar tsaro da ta daɗe tana addabar ƙasar.

A ƙarƙashin wannan tsarin, hukumar ƴansandan Najeriya (NPF) za ta ɗauki ’yan sanda 50,000 ƙarin da za a haɗa da adadin da ake da shi yanzu.

Za a buɗe kafar ɗaukar aikin daga ranar 15 ga wannan wata na Disamban zuwa 25 ga watan Janairun 2026.

Wannan mataki ya biyo bayan wani shiri da gwamnatin ta soma tun farko na ɗaukar jami’an tsaro 30,000, waɗanda suka haɗa da ma’aikatan gidajen gyaran hali, ma’aikatan kula da iyakoki (Immigration), da wasu sassan tsaro daban-daban.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da matsalar tsaro ta ƙara ta’azzara a sassan Najeriya

Post masu alaƙa

Sojojin Najeriya sun daƙile yunƙurin garkuwa da mutane tare da ceto mutum 23

Dan KAROTA da direba ya buge ya gudu Nasiru Abdullahi Mai Jihadi ya rasu ya bar mata 2 da ‘ya’ya 12.

An kama budurwa ‘yar shekara 15 kan safarar miyagun kwayoyi a Delta.