Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ƙaddamar da tallafin rabon kayan abinci na Ramadan ga magidanta 300,000 a faɗin ƙananan hukumomi 27 da ke jihar.
Rabon abincin an ƙaddamar da shi ne a filin wasa na Ramat Square da ke babban birnin jihar Maiduguri, an tsara shi ne don rage wahalhalun tattalin arziki da mazauna karkara ke fuskanta a lokacin watan Ramadan mai alfarma.
A ƙarƙashin shirin, kowane magidanci mai cin gajiyar zai sami buhun shinkafa ɗaya, buhun gero ɗaya da kuma kilo 10 na sukari – muhimmancin rabon kayan abincin nada nufin rage wa iyalan da ke fama da hauhawar farashin kaya.
A jawabin da ya yi wa taron masu cin gajiyar da shugabannin al’umma, Zulum ya yi gargaɗi mai tsauri game da karkatar da kayan agajin.
“Don haka duk wani jami’i da aka samu yana karkatar da waɗannan kayayyaki ga buƙatunsa zai fuskanci fushin doka.”
Gwamnan ya kuma umarci al’ummomin da ke gudanar da azumin Ramadan na wannan shekarar da su amfana da wannan kyautar, yana mai jaddada tsarin gwamnatinsa na haɗa kan jama’a.
“