Daga: Muhammad Inuwa Ibrahim
Shugaban kungiyar JIBWIS na kasa, Sheik Dr. Abdullahi Bala Lau, ya ziyarci fadar mai martaba sarkin Hadejia, Dr. Abubakar Adamu Maje CON, a jiya juma’a.
- Kamfanin Meta Ya Yi Rashin Nasara A Kotu Kan Karya Dokoki A Nijeriya
- Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Sabon Shugaban Gidan Gyaran Hali Ya Mayar Da Hankali Wajen Gyara Tarbiyar Daurarru
Wannan ne karo na uku da kungiyar Izila ta kasa takai irin wannan ziyarar fadar sarkin Hadejia don yin da’awa sakamakon kawo babbar jami’ar musulinci ta duniya Assalam Global University dake Hadejia a jihar Jigawa.
Cikin wadanda suka yiwa, Bala Lau, rakiya sun hada da skaataren kungiyar, Sheik Muhammed Kabiru Haruna Gombe da kuma sauran manyan malamai dake fadin Nijeriya.
A wajabinsa Shiek Abdullahi Bala Lau, yayi fatan jami’ar zata kawo sauye-sauye masu yawa ga al’ummar musulmin duniya baki daya.
Mai martaba sarkin Hadejia, Dr. Abubakar Adamu Maje CON,ya godewa musu bisa wannan ziyara da suka kai masa har fadarsa.