Home » Shugaba Tinubu Ya Bada Umurnin A Kamo Makasan ‘Yan Arewa A Edo 

Shugaba Tinubu Ya Bada Umurnin A Kamo Makasan ‘Yan Arewa A Edo 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Shugaban ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi Allah-wadai da kisan mutane 16 da aka yi a jihar Edo, yana mai umartar hukumomin tsaro da su kamo waɗanda suka yi wannan mummunar aika-aikar.

“Ba za a bari miyagu su ci gaba da zubar da jinin ‘yan Nijeriya ba tare da hukunta su ba.

“Dole ne a yi adalci,” a cewar wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar.

Umurnin na shugaba Tinubu na zuwa ne a dai-dai lokacin da batun ke ƙara ɗaukar ɗumi a sassan Najeriya, musamman Arewacin ƙasar in da jama’ar da aka yi wa kisan gillar suka fito.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?