Shugaban ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi Allah-wadai da kisan mutane 16 da aka yi a jihar Edo, yana mai umartar hukumomin tsaro da su kamo waɗanda suka yi wannan mummunar aika-aikar.
“Ba za a bari miyagu su ci gaba da zubar da jinin ‘yan Nijeriya ba tare da hukunta su ba.
“Dole ne a yi adalci,” a cewar wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar.
- Kwankwaso Da Atiku Sun Fusata Kan Kisan ‘Yan Arewa A Edo
- Mutane 16 Da Aka Kashe A Edo ’Yan Jihar Kano Ne — Amnesty
Umurnin na shugaba Tinubu na zuwa ne a dai-dai lokacin da batun ke ƙara ɗaukar ɗumi a sassan Najeriya, musamman Arewacin ƙasar in da jama’ar da aka yi wa kisan gillar suka fito.