• Home  
  • Shugaba Tinubu Ya Bada Umurnin A Kamo Makasan ‘Yan Arewa A Edo 
- Babban Labari - Labarai - Siyasa

Shugaba Tinubu Ya Bada Umurnin A Kamo Makasan ‘Yan Arewa A Edo 

Shugaban ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi Allah-wadai da kisan mutane 16 da aka yi a jihar Edo, yana mai umartar hukumomin tsaro da su kamo waɗanda suka yi wannan mummunar aika-aikar.

Shugaban ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi Allah-wadai da kisan mutane 16 da aka yi a jihar Edo, yana mai umartar hukumomin tsaro da su kamo waɗanda suka yi wannan mummunar aika-aikar.

“Ba za a bari miyagu su ci gaba da zubar da jinin ‘yan Nijeriya ba tare da hukunta su ba.

“Dole ne a yi adalci,” a cewar wata sanarwa da mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar.

Umurnin na shugaba Tinubu na zuwa ne a dai-dai lokacin da batun ke ƙara ɗaukar ɗumi a sassan Najeriya, musamman Arewacin ƙasar in da jama’ar da aka yi wa kisan gillar suka fito.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai