Shugaba Tinubu Ya Wuce Faransa Daga Birtaniya 

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya wuce birnin Paris na ƙasar Faransa daga birnin Landan na Birtaniya a yau Juma’a.

Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin siyasa, Ibrahim Kabir Masari ne ya bayyana hakan bayan ya kai masa ziyara a Landan.

Masari ya bayyana hakan ne a wani saƙo a shafinsa na X inda ya ce:

“Yau na yi nasarar kai wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ziyara a gidansa da ke Birtaniya, inda muka yi tattaunawa mai amfani,” “Daga nan kuma sai muka wuce birnin Paris na Faransa domin yin wasu ayyukan masu muhimmanci.”

Tun a ranar 2 ga watan Oktoba ne dai Tinubu ya tafi Birtaniya domin yin hutun mako biyu, kamar yadda fadarsa ta bayyana a lokacin, amma ba ta ce zai je Faransa ba.

Fadar ta ce, Tinubu zai koma gida da zarar hutun ya ƙare.

 

Post masu alaƙa

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu

Ƴan sanda sun fara bincike kan mutuwar wanda ake zargi da sokawa matashi Wuƙa a Kano

Babachir Lawal ya fita daga ADC