Shugaba Tinubu Ya Wuce Faransa Daga Birtaniya 

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya wuce birnin Paris na ƙasar Faransa daga birnin Landan na Birtaniya a yau Juma’a.

Mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin siyasa, Ibrahim Kabir Masari ne ya bayyana hakan bayan ya kai masa ziyara a Landan.

Masari ya bayyana hakan ne a wani saƙo a shafinsa na X inda ya ce:

“Yau na yi nasarar kai wa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ziyara a gidansa da ke Birtaniya, inda muka yi tattaunawa mai amfani,” “Daga nan kuma sai muka wuce birnin Paris na Faransa domin yin wasu ayyukan masu muhimmanci.”

Tun a ranar 2 ga watan Oktoba ne dai Tinubu ya tafi Birtaniya domin yin hutun mako biyu, kamar yadda fadarsa ta bayyana a lokacin, amma ba ta ce zai je Faransa ba.

Fadar ta ce, Tinubu zai koma gida da zarar hutun ya ƙare.

 

Post masu alaƙa

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 26 a Borno

Tinubu ya tafi hutun mako uku

Gwamnatin Kwara ta haɗa mutum 146 da aka sace a Woro da iyalansu