Home » Sojoji Sun Halaka Ƴan Ta’adda 80 A Katsina

Sojoji Sun Halaka Ƴan Ta’adda 80 A Katsina

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Rundunar sojojin saman Najeriya ta ce ta halaka sama da ƴan ta’adda 80, a wani ƙauyen jihar Katsina. 

Ta ce ta yi nasarar ƙone baburansu 45 sakamakon luguden wutar da ta yi musu a daren ranar Asabar ɗin da ta gabata.

Wannan na ƙunshe a cikin wata sanarwa da rundunar sojin sama ta Najeriya ta fitar a ranar Litinin.

Sanarwar da daraktan hulɗa da jama’a da yaɗa labarun rundunar sojin, Edward Gabkwet ya sanyawa hannu, ta ce an kai harin ne a wata maɓoyar ƴan bindigar da ke ƙauyen Gidan Kare a ƙaramar hukumar Faskari.

Sanarwa sojojin ta ce ta kai harin ne a daren ranar Asabar a lokacin da ta samu rahoton cewa ƴan ta’adda kimanin 100 sun kai hari a wani ƙauyen da ke da nisan kilomita biyar daga Gidan Kare, inda suka ƙone gidajen jama’a.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?