Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 26 a Borno

Rundunar Sojin Najeriya ta ce ta kashe aƙalla ’yan ta’adda 26 tare da lalata babura 10 a wani samame da ta kai bayan daƙile harin da mayakan suka kai wa sojoji a Kukawa da ke Jihar Borno.

Mai magana da yawun Rundunar Operation HADIN KAI, Kyaftin Mohammed Goni, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar, 29 ga Agusta, 2026, inda ya ce sojojin ƙasa da na sama sun bi sawun maharan bayan sun fatattake su daga Kukawa.

Ya ce harin ya fara ne da misalin ƙarfe 10:50 na daren Juma’a, 28 ga Agusta, lokacin da ’yan ta’addan suka kai hari kan sojojin Rundunar 101 ta Musamman da ke Kukawa.

A cewarsa, sojojin sun mayar da martani da harbi kai tsaye da kuma na nesa, lamarin da ya tilasta wa maharan komawa yankin Cross Kauwa.

Ya ce an kashe ’yan ta’adda da dama a fafatawar farko, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga.

Kyaftin Goni ya ce daga bisani sojojin ƙasa sun gano wasu gawarwakin ’yan ta’addan, yayin da wasu daga cikin waɗanda suka tsere suka yi yunƙurin tserewa a kan babura.

Ya ce duk da mawuyacin yanayi, dakarun sama na Operation HADIN KAI sun kai hare-hare kan ’yan ta’addan da suka ɓuya a ƙarƙashin bishiyoyi, inda aka ƙiyasta cewa an kashe 10 daga cikinsu a hare-haren farko na sama.

A cewarsa, na’urorin leƙen asiri da sa ido sun gano wasu babura kusan 20 da ke ɗauke da mayaƙan da suka tsere, lamarin da ya ba dakarun damar bin sawunsu tare da kai musu hare-hare.

Ya ce wani harin sama da aka kai a kan hanyar Tunbuns zuwa Kangarwa ya kashe wasu ’yan ta’adda 15 tare da lalata babura 10.

Daga baya, sojojin ƙasa sun gano wasu babura biyu, inda suka kashe wani da ake zargi ɗan ta’adda ne yayin ƙarin bincike.

Rundunar ta ce an kuma gano harsasai iri-iri da wasu kayayyaki a yankin, inda ta ce an gudanar da aikin haɗin gwiwar ne domin hana maharan sake taruwa bayan sun gaza cimma burinsu na kai hari a Kukawa.

Rundunar ta ƙara da cewa jami’an soji huɗu sun samu raunuka a fafatawar, amma babu wanda ke cikin mawuyacin hali da zai jefa rayuwarsa cikin haɗari.

An kwashe jami’an zuwa wani wurin jinya ta jirgin sama, inda rundunar ta ce suna samun sauƙi.

Ƙaramar Hukumar Kukawa, da ke gaɓar yammacin Tafkin Chadi, na da muhimmiyar rawa a dabarun tsaro saboda kusancinta da hanyoyin da ke haɗa al’ummomin yankin tafkin.

Rundunar ta ce dakarunta sun fara sake tsara ayyukansu na bincike domin tantance ɓarnar da aka samu sakamakon harin.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Kwara ta haɗa mutum 146 da aka sace a Woro da iyalansu

Yan sanda sun gargadi ’yan siyasa kan kalaman tashin hankali a Kano.

Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Wata Mata Mai Shekaru 30 Da Katunan ATM 88