Gwamnan jihar Zamfara ya rage yawan ma’aikatun jihar daga 28 zuwa 16
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya rattaba hannu kan rage ma’aikatun gwamnatin jihar daga 28 zuwa 16, don Farfado da tattalin arzikin Jihar.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya rattaba hannu kan rage ma’aikatun gwamnatin jihar daga 28 zuwa 16, don Farfado da tattalin arzikin Jihar.
Wannan naɗi nata ya biyo bayan aikewa da sunanta da gwamna Engr. Abba Kabir Yusuf ya yi a cikin wata wasika ga majalisar dokokin jihar Kano wanda shugaban majalisar, Ismail Falgore, ya karanta ta a gaban majalisar a jiya.
Hukumar karbar Korafe-Korafe da Yaki da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), ta ce binciken kwakwaf din da aka gudanar ya nuna bidiyon Dalar da ake zargin tsohon gwamnan Jihar, Abdullahi Umar Ganduje da karbar na goro gaskiya ne.
Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin sababbin shuwagabannin hukumomin KAROTA, REMASAB da REDIYON KANO da kuma wasu da za su shiga cikin masu bada shawarwari na musamman a gwamantinsa.
Hukumar karɓar korafe-korafe da hana cin hanci da rashawa ta jihar kano karkashin jagorancin Barr. Muhuyi Magaji Rimin Gado ta kwato wasu motocin kwashe shara guda goma 12 mallakin gwamnatin jiha.
Mahauta da masu sana’ar sayar da fatu a jihar Kano sun koka game da yadda karancin yin layya daga ya shafi sana’arsu da kuma yiwuwar a hakan ya shafi yawan fatocin dabbobi da ake samu a kowacce babbar sallah.
A jiya Juma’ar nan ne aka ga Hukumar Tsara birane ta jahar kano KNUPDA ta shafa Jan fenti ga Dogayen gine-ginen da aka yi tare da ba su wa’adin kwance gine-ginen bisa hujjar cewa an yi su akan Badala.
Zaɓaɓɓen gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, ya tabbatar da aniyar gwmanatinsa sake fasalin kasuwannin jihar Kano tare da yin aiki ba tare da nuna bambanci ba.
Kwamishinan ‘yansandan Jihar Zamfara, Muhammad Bunu, a madadin babban sufeton ‘yansanda na kasa, Usman Alkali Baba ya gabatar da check ɗin kudi na Naira miliyan 23,574,204 ga iyalai da ‘yan uwa 21 na jami’an ‘yansanda da suka rasa rayukansu a bakin aiki.
majalisar dokokin jihar Kano ta nuna damuwa kan matsalolin satar waya da sane da shan miyagun kwayoyi da ma waɗansu laifukan da ke barazana ga zaman lafiyar jihar.