Nigeria

Dole ne fasinjoji su kashe waya bayan shiga jirgi – NCAA

Sakamakon wasu abubuwa marasa daɗi da suka auku a filayen tashi da saukar jiragen sama na baya-bayan nan, hukumar kula da sufurin jiragen sama ta Najeriya (NCAA) ta bayar da umarnin cewa dukkan fasinjojin su kashe wayarsu a lokacin da suka shiga jirgin sama. A wani taron manema labarai a Abuja ranar Talata, Darakta Janar […]

Read more

Amurka Ta Yaba Wa Najeriya Bisa Kama Jagororin Ansaru

Ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya ya yaba da kama fitattun shugabannin ƙungiyar Ansaru da jami’an tsaronta suka yi. A ranar Asabar ne gwamnatin Najeriya ta ce jami’an tsaronta sun kama ƴan ƙungiyar ta Ansaru, waɗanda take zargi da kitsa fasa gidan yarin kuje a shekarar 2022 har suka tseratar da wasu fursunoni. Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar […]

Read more

Sarkin Zuru Ya Rasu

Sarkin Zuru Manjo Janar Muhammadu Sani Sami II mai ritaya ya rasu yana da shekara 81 da haihuwa. Sakataren yaɗa labarai na gwamantin jihar Kebbi, Ahmed Idris, ya faɗa cikin wata sanarwa cewa sarkin ya rasu ne a wani asibiti da ke birnin Landan ranar Asabar da dare. Sarkin tsohon gwamnan mulkin soja ne na […]

Read more

Yadda Aka Kama Yan Dabar Siyasa 288 A Kano

  Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta kama mutum 288 da ake zargin ’yan daba ne a lokacin zaɓen cike gurbi da aka gudanar a jihar. Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce an kama mutanen da makamai masu hatsari, ciki har da bindigogi ƙirar gida, wuƙaƙe da adduna. Ya bayyana cewa an yi […]

Read more

An Sake Ceto Matafiya 10 Da Aka Sace A Kogi

Jami’an tsaro sun kuɓutar da wasu fasinjoji 10 da aka yi garkuwa da su a hanyar Itobe – zuwa Ochadamu – Anyigba a Ƙaramar hukumar Ofu a Jihar Kogi. Fasinjojin da aka kuɓutar an yi garkuwa da su ne a ranar 11 ga watan Agusta a ƙauyen Ugbakpedo da ke kan titin, lokacin da wata […]

Read more

Sojojin Najeriya Sun Musanta Miƙa Wuyan Bello Turji

Shelkwatar tsaron Najeriya ta musanta rahotanni da ke cewa riƙaƙƙen ɗan fashin dajin nan wanda ya yi ƙaurin suna, Bello Turji ya miƙa wuya ga sojojin ƙasar. Daraktan yaɗa labarai da aikace-aikacen shelkwatar tsaron, Manjo-Janar Markus Kangye ne ya bayyana haka yayin tattaunawa da manema labarai a yau Alhamis. “Maganar ita ce Bello Turji bai […]

Read more