Tag: Nigeria

Babban Labari

Ƙaramar ministar ƙwadagon Najeriya ta yi murabus

Ƙaramar Ministar kwadagon Najeriya Nkeiruka Onyejeocha ta yi murabus daga muƙaminta. Ta sanar da murabus ɗin nata ne a shafinta na X, inda ta miƙa godiyarta ga shugaba Bola Ahmed Tinubu wanda ya bata dama ta yi aiki da gwamnatinsa. Ta bayyana ajiye muƙamin nata a matsayin matakin rufe wani gagarumin babi na rayuwarta a […]

Babban Labari

Tarko INEC ke son ɗana mana kuma ba za mu kamu ba – ADC

Jama’iyyar adawa ta ADC ta haɗakar ƴan adawar Najeriya ta zargi hukumar zaɓen ƙasae INEC ta naɗa mata tarko ta hanyar hanyar yunƙurin dakatar da ita daga gudanar tarukanta domin zaɓen shugabanninta. ADC – tsagin David Mark – ta jaddada aniyar ci gaba da tsare-tsarenta na gudanar da zaɓukan shugabanninta na jihohi da babban taron […]

Babban Labari

Tinubu ya gana da shugaban Chadi

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya karɓi baƙucnin shugaban Chadi Idriss Déby a ranar Alhamis. Sun yi ganawar ce cikin sirri a fadar shugaban Najeriya da ke Abuja, inda ake sa ran sun tattauna kan batutuwa da suka shafi tattalin arziki da kuma haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu. Ganawar na zuwa ne kafin tafiyar shugaba […]

Babban Labari

Harin Iran ya jikkata sojojin Amurka 12 a Saudiyya

Rahotanni sun ce wani harin makami mai linzami daga Iran ya jikkata sojojin Amurka 12 a wani sansanin soji da ke Saudiyya. Jami’ai sun shaida wa abokiyar hulɗar BBC, wato CBS, cewa wasu daga cikin sojojin sun samu munanan raunuka a sansanin jiragen sama na Yarima Sultan. Harin ya kuma lalata wasu jiragen sojin saman […]

Babban Labari

Mahaifiyar Nasir El-Rufai ta rasu

Mahaifiyar tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai mai suna Hajiya Umma El-rufai ta rasu. Ɗan tsohon gwamnan, Bello El-Rufai ne ya sanar da rasuwar a ranar Juma’a, inda ya rubuta a shafinsa na Facebook cewa, “Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un. Ina sanar da al’umma cewa Allah ya yi wa kakata, Hajiya Umma El-Rufai […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai