Home » Tanka Ta Yi Ajalin Sama Da Mutane 60 A Neja

Tanka Ta Yi Ajalin Sama Da Mutane 60 A Neja

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Rahotanni daga Jihar Neja na cewa aƙalla mutane 60 ne suka mutu yayin da wasu da dama suka jikkata bayan da wata tanka ta kife a kusa da Dikko Junction da ke kan hanyar Abuja zuwa Kaduna a wanda ke a Jihar Neja.

Kwamandan Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC) shiyyar Neja, Kumar Tsukwam, ya ce akasarin waɗanda abin ya rutsa da su talakawa ne mazauna yankin da suka yi gaggawar ɗiban man da ya zube bayan motar ta kife.

“Mutane da yawa sun taru domin ɗiban mai duk da ƙoƙarin da aka yi na hana su.

“Kwatsam, sai tankar ta kama wuta, ta kuma kona wata motar dakon mai, ya zuwa yanzu an kwashe gawarwaki 60 da aka gano a wurin.”

Gwamnan jihar Neja Umaru Bago ya bayyana lamarin a matsayin abin damuwa a sanarwar da sakataren watsa labaransa, Bologi Ibrahim ya fitar.

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?