Tinubu Ya sauya Sunan Jami’ar Maiduguri Zuwa Muhammadu Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami’ar Maiduguri zuwa Muhammadu Buhari, marigayi shugaban Najeriya.

Tinubu ya sanar da haka ne a taron majalisar zartaswa da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

“Kafin mu fara addu’o’i domin karrama Buhari, ina sanar da ku cewa mun sauya sunan Jami’ar Maiduguri zuwa Muhammadu Buhari,” in ji Tinubu.

Manyan jami’an gwamnati da dama ne suka halarci taron addu’o’in, ciki har da wasu daga cikin ƴaƴan marigayin.

Post masu alaƙa

Tinubu da gwamnoni sun kafa kwamitin lalubo hanyoyin rage tsadar sufuri

Yan sanda sun gargadi ’yan siyasa kan kalaman tashin hankali a Kano.

Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Wata Mata Mai Shekaru 30 Da Katunan ATM 88