Kotu Ta Bada Umarnin Tsare Matashin Da Ake Zargi Da Furta Kalmar Damfara Kan A . A Zaura A Facebook

Babbar kotun Tarayya mai lamba 3 da ke zamanta a Gyadi-gyadi, karkashin mai shari’a Simon Amobeda, ta aike da wani matashi mai suna Ahmad Ilyasu gidan ajiya da gyaran hali bisa zarginsa da laifin batawa Abdulsalam Abdulkareem AA Zaura, suna a kafar sada zumunta ta Facebook.

Tunda fari dai kunshin zargin ya ayyana cewa matashin ya yi amfani da shafin nasa na Facebook, inda ya kira A-A Zaura, da cewa Dan Damfara ne, zargin da matashin ya musanta.

Matashi Ahmad Ilyasu, ya ce bai san da batun zargin da ake yi masa ba, a nan ne lauyan da yake kare shi ya roki kotun da ta bada belinsa kasancewar zargin da ake yi wa matashin ya fada cikin zarge-zargen da za a iya bayar da Beli.

Sai dai bangaren masu kara sun yi suka akan rokon bada belin, inda suka ce suna tsoron ka da a bayar da belin matashin ya tserewa shari’a, ko kuma ya sake aikata makamancin laifin a don haka ne suka yi sukar.

Kotun ta sanya ranar 22 ga wannan wata na Yulin 2025, domin ta yi kwarya-kwaryar hukunci akan batun bayar da belin ko kuma akasin hakan

Post masu alaƙa

Tinubu ya gaji, ya kamata ya yi ritaya – Peter Obi

Kwalejin Fasaha ta Kogi ta dakatar da lakcarori 7 kan cin zarafin ɗalibai

Najeriya ta yi martani kan kisan ɗan ƙasarta a Afrika ta Kudu