Victor Osimhen Ne Kan Gaba A Yawan Zura Kwallaye A Champions League

Ɗan wasan gaba na Nijeriya, Victor Osimhen, ya sha gaban fitattun ‘yan wasa irin su Erling Haaland, Harry Kane, da Kylian Mbappé a yawan zura ƙwallaye a gasar Champions League ta bana.

Osimhen ya cimma wannan nasarar ce bayan ya zura ƙwallaye uku rigis a ragar Ajax a wasan zagaye na huɗu na gasar.

Wannan ya kai adadin ƙwallayensa zuwa shida, yayin da Haaland, Kane da Mbappé ke da ƙwallaye biyar-biyar kowannensu.

A watan da ya gabata, Osimhen ya kuma zura ƙwallaye uku a ragar Jamhuriyyar Benin a wasan neman tikitin shiga gasar Kofin Duniya ta 2026, abin da ya ƙara masa farin jini a duniya.

Ɗan wasan da yanzu haka yake bugawa Galatasaray na Turkiyya, yana jan hankalin manyan kungiyoyi da dama a Turai, ciki har da Barcelona, wadda ke neman ƙwararren mai zura ƙwallaye domin cike gibin da ke cikin tawagarta.

 

Post masu alaƙa

Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Wata Mata Mai Shekaru 30 Da Katunan ATM 88

Najeriya ta ƙaddamar da yaƙi ta sama kan ƴan fashin daji

Abubuwa shida da suka sauya tun bayan zaɓen Najeriya na 2023