Tinubu Ya Rantsar Da Sababbin Ministoci

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya rantsar da Bernard Mohammed Doro da Kingsley Tochukwu Udeh a matsayin ministoci.

Tun mako biyu da suka wuce ne majalisar tarayya ta amince da Mista Doro domin maye gurbin Farfesa Nentawe Yilwatda daga jihar Filato, wanda ya zama shugaban jam’iyyar APC na ƙasa mai mulkin Najeriyar.

Sai a yau Alhamis ne kuma majalisar ta amince da naɗin Kingsley Tochukwu Udeh wanda zai maye gurbin Uche Nnaji daga jihar Enugu, wanda ya sauka daga muƙamin ministan kimiyya bayan zarge-zargen gabatar da shaidar karatu ta bogi.

Tinubu ya rantsar da ministocin ne jim kaɗan kafin fara taron majalisar zartarwa a fadar shugaban da ke Abuja.

Post masu alaƙa

Alarammomi sun amince da tsarin haɗa ilimin boko da na addini a Jigawa

Gwamnati za ta mayar da yara 5,000 makaranta a Jigawa

Ba mu ƙarƙare batun sauya kayan NYSC ba – Ministan Matasa