Wani sanata daga Kano ya raba wa dalibai 200 tallafin kudin makaranta

Daliban jami’ar Bayero su 200 sun sami tallafin kudin makaranta da Sanatan Kano ta tsakiya sanata Rufa’i Sani Hanga ya biya musu.

Wannan na zuwa ne yayin da ɗalibai ke neman ɗauki daga gwamnati da masu hannu da shuni domin biyan kudin makaranta.

Ya zuwa yanzu dai rahotanni sun nuna cewa, ‘yan majalisun tarayya na Bichi da Dambatta/Makoda da Wudil/Garko ne suke kan gaba wajen  biya wa daliban yankinsu kudin makaranta bayan ƙarin kudin makaranta da jami’o’i suka yi.

Dalibai da dama na cikin fargabar gaza cigaba da karatun jami’a a sassan Kano bisa rashin kudin da za su biya kudin makarantunsu tun bayan karin kudin da aka yi.

Post masu alaƙa

Kwalejin sojan ruwa dake Dawakin-Tofa ta kara karfafa hadin gwiwar aiki tare da rundunar yan sandan Kano.

Sojojin Najeriya sun ceto mutane 9 daga masu garkuwa a Kogi.

Kotu tsare mutane biyu da ake zargi da rushe Gadar Watari da yanka filaye ba bisa ka’ida ba a Kano.