Wata Babbar Kotu Ta Shiga Tsakanin Tsohon Gwamnan Kano, Ganduje da Muhyi Magaji

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a nan Jihar Kano, ta hana gayyata ko kama tsohon gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje domin bincikarsa kan zargin karbar cin hanci da rashawa. 

A ranar Alhamis ne dai Hukumar karbar korafe-korafe da hana cin hanci da rashawa ta Jihar Kano ta ce ta aika takardar sammaci ga tsohon gwamnan a kan ‘bidiyon dala’.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar, na cewa ta gayyaci Ganduje ne domin ya je ya wanke sunansa game da binciken da ake yi.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr