Jihar Neja: Wasu Mutane 11 Sun Rasa Rayukansu a Wani Haɗarin Mota

Kasa da sa’o’i 24 da rasa rayukan mutane 11 a hanyar Mokwa zuwa Lapai a Jihar Neja, wasu mutane 24 sun mutu a wani hatsarin mota da auku a hanyar Kutigi zuwa Bida a jihar.

Wani ganau ya shaida wa MUHASA  cewa hatsarin ya auku ne da tsakar daren ranar Talata a kauyen Etsuworo, inda wata babbar mota ta taso daga Zariya zuwa Jihar Legas.

Kwamandan hukumar kiyaye hadura ta kasa (FRSC) a jihar, Kumar Tsukwam, ya tabbatar da cewa mutane 24 ne suka mutu a hatsarin, kuma an garzaya da wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Kutigi, da ke hedikwatar karamar hukumar Lavun ta jihar.

Post masu alaƙa

Kwamitin zaman lafiya ya gana da yan sandan Kano kan zaɓen 2027.

An kashe kwamandojin ’yan bindiga biyu a Katsina

Yan Sandan a Kano sun kama mutane 244, ciki har da 117 da ake zargi da fadan daba.