Jihar Neja: Wasu Mutane 11 Sun Rasa Rayukansu a Wani Haɗarin Mota

Kasa da sa’o’i 24 da rasa rayukan mutane 11 a hanyar Mokwa zuwa Lapai a Jihar Neja, wasu mutane 24 sun mutu a wani hatsarin mota da auku a hanyar Kutigi zuwa Bida a jihar.

Wani ganau ya shaida wa MUHASA  cewa hatsarin ya auku ne da tsakar daren ranar Talata a kauyen Etsuworo, inda wata babbar mota ta taso daga Zariya zuwa Jihar Legas.

Kwamandan hukumar kiyaye hadura ta kasa (FRSC) a jihar, Kumar Tsukwam, ya tabbatar da cewa mutane 24 ne suka mutu a hatsarin, kuma an garzaya da wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Kutigi, da ke hedikwatar karamar hukumar Lavun ta jihar.

Post masu alaƙa

Babandede Ya Ziyarci Iyalan Hon. Laushi, Ya Ba Su Tallafi

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM