Home » ’Yan Bindiga Sun Harbe Malamin Jami’a Sun Sace Motarsa

’Yan Bindiga Sun Harbe Malamin Jami’a Sun Sace Motarsa

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Wasu ’yan bindiga sun harbe malamin Jami’ar Nnamdi Azikiwe (UNIZIK), Dokta Osita Chinedu, har lahira a daren Litinin a Jihar Anambra.

Wadan da abin ya faru a gabansu sun bayyana cewa ’yan bindigar sun tsayar da motar malamin, kafin suka harbe shi kuma suka tsere da motarsa ƙirar Toyota Corolla.

Kawo yanzu Rundunar ’yan sandan Jihar Anambra, ta tabbatar da lamarin, tare da bayyana cewa ta fara bincike domin gano wadan da suka aikata mummunan aikin.

’Yan sanda sun buƙaci duk wanda ke da bayanan da za su taimaka wajen kama masu laifin ya kai rahoto zuwa ofishin ’yan sanda mafi kusa da shi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?