Yan Sanda Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Lalata Taransifoma A Hadejia

Rundunar yan sandan jihar Jigawa, ta samu nasarar kama wasu mutane da ake zargi lalata Taransifoma, a karamar hukumar Hadejia.

Kakakin rundunar yan sandan jihar SP Shisu Lawan Adamu, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar.

Sanarwar ta ce an kama batagarin lokacin da suke barnata na’urar wutar lantakin, wadanda suka fito daga jahohin Kano, Bauchi da kuma Jigawa.

Haka zalika ana zargin sun kware wajen lalata taransifoma tare da siyar da ita a garuruwa dabanm-daban.

Wadanda ake zargin sun hada sun hada Haruna Musa dan shekaru 36 , Hussaini Innocent, Abubakar Yakubu , Zakariyya Mohammed, Mamman Danladi , Khalifa Yahaya, Ibrahim Mohammed,  Ali Ibrahim.

Hakazalika, an kara kama wasu matasan a garin Bamaina a lokacin da suke kona wayar wutan lartarki a wata makaranta wadda kudin wayar yakai naira miliyan bakwai (7).

SP Shisu Adamu, ya kara da cewa tuni sun gurfanar da wasu daga cikin matasan, a gaban kotu, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike don kamo sauran da suka gudu da kuma masu siyan kayan satar.

Post masu alaƙa

Ƴan sanda sun fara bincike kan mutuwar wanda ake zargi da sokawa matashi Wuƙa a Kano

Babachir Lawal ya fita daga ADC

DSS ta kama mutane 5 da ake zargi da sace ɗaliban makarantar St. Mary’s Pipiri a jihar Neja