Home » Yan Sanda Sun Kama Matar Da Ake Zargi Da Koyawa Matasa Laifuka A Jigawa.

Yan Sanda Sun Kama Matar Da Ake Zargi Da Koyawa Matasa Laifuka A Jigawa.

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Rundunar yan sandan jihar Jigawa, ta samu nasarar kama wata matashiya, mai suna Shamsiyya Muhammad yar shekaru 28 mazauniyar Gidan Ruwa, bisa zarginta da koyawa matasa maza da mata hanyoyin aikata laifuka.

Kakakin rundunar yan sandan jihar Jigawa, SP Shiisu Lawan Adamu, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da aikewa da manema labarai.

Sanarwar ta ce an kamata ne lokacin da jami’an yan sanda suke gudanar da sintiri har suka gano sinki-sinki na tabar Wiwi guda 18 da sauran miyagun kwayoyi da aka samu a wajen ta.

Mukadadashin kwamishinan yan sandan jihar, DCP Murtala Tijjani, ya yabawa dakarunsu da jami’an bijilanti bisa jajircewar su wajen yin aiki tare.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?