Rundunar yan sandan jihar kano, ta samu nasarar kama karin mutrane 10 da ake zargi da siyan baburan sata bayan kama wanda ake zargi na farko da satar Baburan jama’a.
Kakakin rundunar yan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai, a ranar Alhamis din nan.
- Tarihi Ba Zai Taɓa Mantawa Da Buhari Ba – Bisi Akande
- CP Ibrahim Bakori Ya Roki Gwamnatin Kano Ta Cika Alkawarin Da Ta Yiwa Tubabbun Yan Daba.
Sanarwar ta ce an samu karin baburan sata guda 7 kuma an mayar wa da mamallakansu bisa jajircewar jami’an yan sandan.
Kwamishinan yan sandan jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya yaba wa dakarunsa bisa jajircewar da suka nuna wajen yaki da aikata laifuka, da kuma kare rayukan al’umma da dukiyoinsu.