‘Yan Sanda Sun Kamo ‘Yan Daba A Kano

Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Kano ta kama mutane 8 cikin wadanda ake zargi sun fito fadan daba tare da jiwa Kansu raunuka, a unguwar kofar Na’isa ranar Alhamis din data gabata.

Kakakin rundunar ƴan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana a shafin sa na Facebook , ayau Asabar.

Rundunar yan sandan ta kuma bayyana damuwa, kan yadda matasan da suka samu raunukan, suka ki sanarwa da yan sanda, don kaisu asibiti a kula da lafiyarsu.

Kiyawa ya kara da cewa jami’an yan sanda sun shiga cikin unguwar, tare da mutane 8 da raunuka a jikinsu da kuma Wukake.

Sanarwar ta ce ana ci gaba da gudanar da bincike don kamo sauran wadanda ake zargi da aikata laifukan.

A ranar Alhamis din data gabata ne , wasu matasa da ake zargin Yan daba ne suka fito,Inda suka tayar da hankalin mazauna yankin da makotansu.

Post masu alaƙa

CP Bakori ya umarci kwamandojin yan sanda su ƙara kaimi wajen yaki da laifuka a Kano.

Kano: Gini Ya Rufta Kan Mutane 16 Ciki Har Da Yara Shida

KACRAN: Babu wani babban rikicin manoma da makiyaya a Yobe