Yanzu-yanzu: Gwamnan Kano Ya Amince da Naɗa Karin Mataimaka 94

A ƙoƙarinsa na tabbatar al’ummar Kano sun samu labarai game da ayyukan gwamnatinsa, gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin karin masu taimaka masa na musamman a matsayin masu ɗaukar rahoto a ma’aikatu da hukumomi daban-daban na jihar Kano.

Gwamnan, ta bakin sakataren yaɗa labaransa, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya bayyana manufar wadannan naɗe-naɗe da cewa wata hanya ce ta samar da bayanai na gaskiya game da ayyuka da tsare-tsaren gwamnatin jihar Kano.

Mataimakan da sun kai 94 waɗanda suka haɗa da wasu ‘yan Jarida da ke aiki da wasu kafofin yaɗa labarai a nan Kano.

DANNA WANNAN RUBUTU DOMIN GANIN SUNAYEN MATAIMAKAN:

Post masu alaƙa

Manjo Janar Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Yan Bindiga

JIBWIS Gwallaga Sun Ziyarci A Sansanin Alhazai Na Jihar Bauchi Domin Bada Agaji

‘Yan Arewa A Jihohin Kudu Sun Koka kan Tsangwama da Wariya Saboda Matsalolin Tsaro