Yanzu-yanzu: Gwamnan Kano Ya Amince da Naɗa Karin Mataimaka 94

A ƙoƙarinsa na tabbatar al’ummar Kano sun samu labarai game da ayyukan gwamnatinsa, gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin karin masu taimaka masa na musamman a matsayin masu ɗaukar rahoto a ma’aikatu da hukumomi daban-daban na jihar Kano.

Gwamnan, ta bakin sakataren yaɗa labaransa, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya bayyana manufar wadannan naɗe-naɗe da cewa wata hanya ce ta samar da bayanai na gaskiya game da ayyuka da tsare-tsaren gwamnatin jihar Kano.

Mataimakan da sun kai 94 waɗanda suka haɗa da wasu ‘yan Jarida da ke aiki da wasu kafofin yaɗa labarai a nan Kano.

DANNA WANNAN RUBUTU DOMIN GANIN SUNAYEN MATAIMAKAN:

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr