• Home  
  • ‘Yar kwallon kafar Najeriya, Asisat Oshoala, ta ba wa mahaifinta hakuri a Instagram
- Wasanni

‘Yar kwallon kafar Najeriya, Asisat Oshoala, ta ba wa mahaifinta hakuri a Instagram

Ƴar wasan kwallon kafa ta Najeriya, Asisat Oshoala ta ce ta san mahaifinta bai ji daɗin irin murnar da ta yi ba bayan cin kwallo a wasan da Najeriya ta doke Australia da ci 3-2.

'Yar kwallon kafar Najeriya, Asisat Oshoala, ta ba wa mahaifinta hakuri a Instagram

Ƴar wasan kwallon kafa ta Najeriya, Asisat Oshoala ta ce ta san mahaifinta bai ji daɗin irin murnar da ta yi ba bayan cin kwallo a wasan da Najeriya ta doke Australia da ci 3-2.

Ƴar wasan Najeriyar ta bayyana haka ne a wani rubutu da ta wallafa a shafinta na Instagram.

Oshoala ce dai ta zura kwallo na uku a wasansu da Australiya a Gasar Kofin Duniya ta Mata ranar Alhamis.

Inda Ta cire rigarta a lokacin da take murnar kwallon da ta ci.

Tun daga lokacin salon murnar da ta yi, ya haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin masoya kwallon kafa a ciki da wajen ƙasar.

Yayin da mutane da yawa ke ganin babu wata matsala game da salon murnar, wasu kuma sun fusata da hakan.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai