Home » ‘Yar kwallon kafar Najeriya, Asisat Oshoala, ta ba wa mahaifinta hakuri a Instagram

‘Yar kwallon kafar Najeriya, Asisat Oshoala, ta ba wa mahaifinta hakuri a Instagram

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
'Yar kwallon kafar Najeriya, Asisat Oshoala, ta ba wa mahaifinta hakuri a Instagram

Ƴar wasan kwallon kafa ta Najeriya, Asisat Oshoala ta ce ta san mahaifinta bai ji daɗin irin murnar da ta yi ba bayan cin kwallo a wasan da Najeriya ta doke Australia da ci 3-2.

Ƴar wasan Najeriyar ta bayyana haka ne a wani rubutu da ta wallafa a shafinta na Instagram.

Oshoala ce dai ta zura kwallo na uku a wasansu da Australiya a Gasar Kofin Duniya ta Mata ranar Alhamis.

Inda Ta cire rigarta a lokacin da take murnar kwallon da ta ci.

Tun daga lokacin salon murnar da ta yi, ya haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin masoya kwallon kafa a ciki da wajen ƙasar.

Yayin da mutane da yawa ke ganin babu wata matsala game da salon murnar, wasu kuma sun fusata da hakan.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?