Yemen: Mutane 85 Sun Rasu, 320 Sun Jikkata Yayin Karɓar Tallafin Kuɗi

Akalla rayukan mutane 85 sun salwanta ciki har da mata da yara yayin da wasu mutanen fiye da 320 suka ji munanan raunika bayan aukuwar wani turmutsitsi a birnin Sanaa da ke karkashin ‘yan tawayen Houthis na kasar Yemen.

Turmutsitsin ya auku ne a yayin da ake rabon taimako na kudade ga marasa karfi a wata makaranta da ke wata Unguwa da ake kira Bab el Yemen kamar yadda wani jami’in gidan asibitin dake karkashi ‘yan tawayen da ke da iko da yankin ya tabbatar.

Har kawo yanzu dai hukumomi ba su yi bayani ba kan musabbabin tirmimutsitsin mafi muni da aka samu a tarihin kasar, kana kuma ba su fitar da alkaluman wadanda lamarin ya ritsa da su ba.

Post masu alaƙa

Sojojin Najeriya sun ceto mutane 9 daga masu garkuwa a Kogi.

Kotu tsare mutane biyu da ake zargi da rushe Gadar Watari da yanka filaye ba bisa ka’ida ba a Kano.

Rundunar yan sandan Kano ta kwato motar da aka sace sannan aka siyar da ita a Nijar